Home General Ku yi koyi da demukradiyyar Ghana – Tinubu ga ECOWAS

Ku yi koyi da demukradiyyar Ghana – Tinubu ga ECOWAS

Shugaba Bola Tinubu ya buƙaci shugabannin ƙungiyar ƙasashen Afirka ta Yamma Ecowas, da su yi koyi tsarin dimokraɗiyyar Ghana, bayan gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da kuma na ƴan majalisar dokoki a ƙasar cikin lafiya da kwanciyar hankali.

An sake zaɓar John Mahama, tsohon shugaban ƙasar a zaɓen ranar 7 ga watan Disamba, inda ya kayar da mataimakin shugaban ƙasar Mahamudu Bawumia. Bawumia ya kira shi tare da yi masa murna tun kafin a sanar da sakamakon zaɓen a hukumance.

Da yake jawabi a wajen taron shugabannin ƙungiyar Ecowas karo na 66 da aka yi a Abuja yau Lahadi, Tinubu ya ce abin da ya faru a Ghana abin koyi ne ga wasu ƙasashe da ke yankin.

Shugaban ƙungiyar ta Ecowas ya kuma yaba wa shugaban ƙasar Ghana mai ci, Nana Akufo-Addo, wanda ya halarci taron a karo na karshe a matsayinsa na shugaba, da irin namijin ƙoƙari wajen shirya sahihin zaɓe.

Tinubu ya kuma yaba wa Senegal ka gudanar da zaɓen ƴan majalisa cikin gaskiya da lumana.

Ya yi kiran haɗin kai tsakanin ƙasashe mambobin Ecowas, musamman wajen kare hakkin ƴan ƙasashensu da kuma samar musu da ababen more rayuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp