Home General PDP ta yi watsi da kasafin kudin 2025

PDP ta yi watsi da kasafin kudin 2025

Jam’iyyar PDP ta soki kasafin kuɗin da shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya gabatar wa majalisar dokokin ƙasar, wanda ta bayyana a matsayin wani abu da ”ba zai yiwu ba” kuma wanda ”babu gaskiya a ciki”.

Sakataren yaɗa labaran PDP Debo Ologunagba, a cikin wata sanarwa a kan kasafin kuɗin, ya ce kasafin kuɗin ya shafi abubuwan da za su ƙara jefa jama’a cikin ƙangin talauci da kuma matsalar tsaro.

Shugaba Tinubu ya gabatarda kasafin na 2025, na naira tiriliyan 49.7 ga majalisar dokokin Najeriya, inda ya sha alwashin bayar da fifiko ga ɓangaren da samar da ayyukan raya ƙasa da fannin kiwon lafiya da kuma ilimi.

Sai dai jam’iyyar PDP mai adawa a ƙasar ta ce gabatar da kasafin kuɗin ba wani abu bane illa alƙawurran da ba za a iya cikawa ba.

Jma’iyyar adawan da zargi gwamnatin shugaba Tinubu da gazawa wajen samar da muhimman abubuwan more rayuwa ga jama’ar ƙasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp