Home General Ana fargabar harin jirgin soji kan lakurawa ya hallaka mutane da dama...

Ana fargabar harin jirgin soji kan lakurawa ya hallaka mutane da dama a Sokoto

Ana fargabar al’umma da dama sun mutu wasu kuma sun jikkata sakamakon wani hari da jirgin yaƙi na soji ya kai kan Lakurawa a wasu ƙauyuka da ke Sokoton Najeriya.

Harin jirgin saman da aka kai kan ƴan ta’addan Lakurawa ya sauka kan alummar wasu ƙauyuka a ƙaramar hukumar Silame ta jihar Sokoto dake arewacin Najeriya

Kauyukan da harin ya shafa sun haɗa da Gidan Sama da Rumtuwa, kuma lamarin ya faru da misalin ƙarfe 7 na safiyar yau Laraba.

Wani mazaunin yankin Silame mai suna Malam Yahya ya ce ƙauyukan na kusa da dajin Surame inda ake zargin maboyar Lakurawa ne da ƴan bindiga.

Wata majiya ta shaidawa Dailytrust cewa sama da mutum 10 ne suka mutu kuma da dama sun jikkata a sakamakon harin jirgin saman yaƙin.

Kawo yanzu babu wata sanarwa  daga hukumomin tsaro kan lamarin.

Shugaban ƙaramar hukumar Silame Alh. Abubakar Muhammad Daftarana ya tabbatar da harin inda ya ce suna bincike kan irin barnar da harin jirgin yaƙin ya yi a ƙauyukan.

Al’ummar ƙauyukan na zaune lami lafiya lokacin da jirgin yaƙin ya yi ruwan wuta kan jama’a

Ya yi wuri na tabbatar da adadin mutanen da harin ya kashe ko suka samu raunuka saboda har yanzu muna tattara bayanai

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp