Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan Ta’adda 80 a jihar Katsina

Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan Ta’adda 80 a jihar Katsina

Gwamnatin jihar Katsina dake arewa maso yammacin Nijeriya ta yabawa dakarun tsaron kasar da suka hadar da Sojojin Operation FANSAN YAMMA dakarun bataliya ta 17 na rundunar sojojin kasa, jami’an tsaro na sa kai da Vigilanti bisa nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga dake Kadoji, Matso-matso, Bagga, Dogon Marke da Takatsaba dake karamar hukumar Jibia.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da PRNigeria ta samu wadda kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Dr. Nasir Muazu ya fitar aka kuma raba manema labarai a jihar.

Wannan dai na zuwa ne bayan wata gagarumar nasara da dakarun suka samu a wani hari da suka kai wa ‘yan bindigar a ranar 4 ga watan janairu, wanda ya kassarar ayyukan ta’addanci a kananan hukumomin Jibia, Batsari da Batagarawa duka a jihar katsina dake fama da matsalar rashin tsaro.

Harin hadin gwiwa ta sama da kasa ya samar da nasarar hallaka ‘yan bindiaga 80, yayin da masu yawa suka tsere da raunikan harbi a jukkunan, inda kuma jamián tsaron sauka tarwata maboyar da wasu cikin makamansu.

Sanarwa ta ce gwamnatin jihar Katsina ta nuna farin cikinta bisa wannan nasarar da aka samu bisa hadin kan jami’an da yunkurinsu na dawo da zaman lafiya a shiyyar arewa maso yamma dake fama da matsalar rashin tsaro.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp