Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan Ta’adda 80 a jihar Katsina

Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan Ta’adda 80 a jihar Katsina

Gwamnatin jihar Katsina dake arewa maso yammacin Nijeriya ta yabawa dakarun tsaron kasar da suka hadar da Sojojin Operation FANSAN YAMMA dakarun bataliya ta 17 na rundunar sojojin kasa, jami’an tsaro na sa kai da Vigilanti bisa nasarar tarwatsa maboyar ‘yan bindiga dake Kadoji, Matso-matso, Bagga, Dogon Marke da Takatsaba dake karamar hukumar Jibia.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da PRNigeria ta samu wadda kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Dr. Nasir Muazu ya fitar aka kuma raba manema labarai a jihar.

Wannan dai na zuwa ne bayan wata gagarumar nasara da dakarun suka samu a wani hari da suka kai wa ‘yan bindigar a ranar 4 ga watan janairu, wanda ya kassarar ayyukan ta’addanci a kananan hukumomin Jibia, Batsari da Batagarawa duka a jihar katsina dake fama da matsalar rashin tsaro.

Harin hadin gwiwa ta sama da kasa ya samar da nasarar hallaka ‘yan bindiaga 80, yayin da masu yawa suka tsere da raunikan harbi a jukkunan, inda kuma jamián tsaron sauka tarwata maboyar da wasu cikin makamansu.

Sanarwa ta ce gwamnatin jihar Katsina ta nuna farin cikinta bisa wannan nasarar da aka samu bisa hadin kan jami’an da yunkurinsu na dawo da zaman lafiya a shiyyar arewa maso yamma dake fama da matsalar rashin tsaro.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp