Home General Gwamnan Kano ya tura sabbin Kwamishinonin da ya Rantsar Zuwa Ma’aikatun da...

Gwamnan Kano ya tura sabbin Kwamishinonin da ya Rantsar Zuwa Ma’aikatun da za suyi aiki

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya tura sabbin Kwamishinoni 7n da ya rantsar zuwa ma’aikatun da zasu kula masa dasu.

Kwamishinan shari’a na jihar kuma babban lauyan Gwamnati, Barista Haruna Isa Dederi ne ya rantsar da sabbin kwamishinonin 7, da sabbin manyan sakatarorin gwamnati guda 6 da aka daga likkafarsu, dama sauran masu baiwa gwamna shawara guda 13.

Sabbin Kwamishinonin dama ma’aikatun da aka tura su sune;

1. Alhaji Shehu Wada Sagagi – Ma’aikatar kasuwanci da zuba jari

2. Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya – Ma’aikatar yada Labarai

3. Dakta Dahir Muhammad Hashim – Ma’aikatar Muhalli

4. Abdulkadir Abdussalam -Ma’aikatar Raya Karkara

5. Dakta Isma’ila Aliyu Dan Maraya – Ma’aikatar Kudi

6. Dakta Gaddafi Sani Yakubu – Ma’aikatar Makamashi

7. Dakta Nura Iro Ma’aji – Ma’aikatar kula da kwangiloli da bibiyar ayyukan gwamnati

A karshe Gwamnan ya taya su murna tare da bukatar su rike gaskiya da amana, domin kiyaye rantsuwar da suka yi na yiwa jama’a aiki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp