Home General Harin ISWAP ya hallaka sojojin Najeriya shida a jihar Borno

Harin ISWAP ya hallaka sojojin Najeriya shida a jihar Borno

Rahotannin daga jihar Borno dake Arewa maso gabashin Nijeriya na bayyana cewa Mayaƙa masu alaƙa da ƙungiyar ISWAP sun hallaka sojojin kasar shida yayin wani hari da suka kai kan sansaninsu, kamar yadda kamfanin yada labarai na AFP ya ruwaito

AFP ya ambato jami’an sojin Najeriya biyu na cewa maharan na ƙungiyar Islamic State West Africa Province (ISWAP) sun far wa sansanin da ke Sabon Gari a ƙaramar hukumar Damboa ranar Lahadi da tsakar dare.

Rahotonni sun ce sun cinna wa sansanin wuta tare da ababen hawan da ke cikinsa.

“An kashe mana sojoji shida a harin na Iswap da suka kai sansanin bayan zazzafar musayar wuta,” kamar yadda ɗaya daga cikin jami’an ya faɗa wa AFP.

Ɗaya jami’in ya ce jirgin sojin sama da aka aika daga binrin Maiduguri, mai nisan kilomita 100, shi ne ya kori maharan.

“Hare-hare ta sama ya kashe ‘yanbindigar da yawa, ya lalata motoci da makamansu,” in ji majiyar ba tare da bayar da yawan adadi ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp