Home General Harin ISWAP ya hallaka sojojin Najeriya shida a jihar Borno

Harin ISWAP ya hallaka sojojin Najeriya shida a jihar Borno

Rahotannin daga jihar Borno dake Arewa maso gabashin Nijeriya na bayyana cewa Mayaƙa masu alaƙa da ƙungiyar ISWAP sun hallaka sojojin kasar shida yayin wani hari da suka kai kan sansaninsu, kamar yadda kamfanin yada labarai na AFP ya ruwaito

AFP ya ambato jami’an sojin Najeriya biyu na cewa maharan na ƙungiyar Islamic State West Africa Province (ISWAP) sun far wa sansanin da ke Sabon Gari a ƙaramar hukumar Damboa ranar Lahadi da tsakar dare.

Rahotonni sun ce sun cinna wa sansanin wuta tare da ababen hawan da ke cikinsa.

“An kashe mana sojoji shida a harin na Iswap da suka kai sansanin bayan zazzafar musayar wuta,” kamar yadda ɗaya daga cikin jami’an ya faɗa wa AFP.

Ɗaya jami’in ya ce jirgin sojin sama da aka aika daga binrin Maiduguri, mai nisan kilomita 100, shi ne ya kori maharan.

“Hare-hare ta sama ya kashe ‘yanbindigar da yawa, ya lalata motoci da makamansu,” in ji majiyar ba tare da bayar da yawan adadi ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp