Home General Gwamnatin Najeriya ta buɗe kwalejin horas da matasa kan ƙirƙirarriyar basira a...

Gwamnatin Najeriya ta buɗe kwalejin horas da matasa kan ƙirƙirarriyar basira a kyauta

Gwamnatin Najeriya ta ce ta ƙaddamar da wani shiri na horar da matasa game da sanin makamar ƙirƙirarriyar basira wato Artificial Intelligence (AI) ta intanet.

Ministan Ƙirƙira, Kimiyya da Fasaha Uche Geoffrey Nnaji ya ce shirin wanda aka ƙaddamar ranar Talata, an yi masa suna AI Academy – wato kwalejin ƙirƙirarriyar basira.

Najeriya ta ƙaddamar da shirin bisa haɗin gwiwa da ƙungiyar ƙasashe rainon Ingila ta Commonwealth.

“AI Academy za ta horar da ɗalibai, da matasa, da ma’aikatan gwamnati wajen shawo kan matsaloli da kuma ƙirƙirar damarmaki ta hanyar amfani da ƙirƙirarriyar basira,” in ji ministan.

Ya ƙara da cewa za a rufe yin rajista a shafin kwalejin ranar 30 ga watan Janairun nan.

Ministan ya ce masu sha’awa na iya a ziyartar wannan adireshin an domin yin rajista.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp