Home General Kotu a Najeriya ta yi watsi da sabbin bukatun da Godwin Emefiele...

Kotu a Najeriya ta yi watsi da sabbin bukatun da Godwin Emefiele ya gabatar mata

Kotun hukunta manyan laifuka da ke jihar Legas a Najeriya, ta yi watsi da bukatar da tsohon gwamnan babban bankin kasara, Godwin Emefiele, ya shigar, yana kalubalantar hukuncin da wata kotu ta yanke bisa zargin badakalar dala biliyan 4.5 da kuma naira biliyan 2.8 da hukumar EFCC ta shigar a kansa.

Mai shari’a Rahman Oshodi, a hukuncin da ya yanke, ya ce kotu na da hurumin gurfanar da Emefiele da wanda ake tuhuma, Henry Omoile.

Sai dai alkalin kotun ya yi fatali da tuhume-tuhume hudu daga cikin tuhume-tuhume 26 da EFCC ta shigar a kan su.

Hukumar EFCC ta gurfanar da Emefiele ne a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume 26, da suka shafi karkatar da kudaden da suka kai dala biliyan 4.5 ba bisa ka’ida ba da kuma Naira biliyan 2.8.

A ranar 12 ga Disamba, 2024, lauyan Emefiele, Mista Olalekan Ojo mai mukamin SAN, ya bayar da hujjar cewa kotun ba ta da hurumin sauraren karar a Legas.

Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta dakatar da Emefiele a matsayin gwamnan CBN a ranar 14 ga Yuni, 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar KatsinaZaben 2027: NDC ta Tsayar da Ɗan Kwankwaso Mataimakin ɗan Takarar Gwamnan KanoKotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja
X whatsapp