Home General Kotu a Najeriya ta yi watsi da sabbin bukatun da Godwin Emefiele...

Kotu a Najeriya ta yi watsi da sabbin bukatun da Godwin Emefiele ya gabatar mata

Kotun hukunta manyan laifuka da ke jihar Legas a Najeriya, ta yi watsi da bukatar da tsohon gwamnan babban bankin kasara, Godwin Emefiele, ya shigar, yana kalubalantar hukuncin da wata kotu ta yanke bisa zargin badakalar dala biliyan 4.5 da kuma naira biliyan 2.8 da hukumar EFCC ta shigar a kansa.

Mai shari’a Rahman Oshodi, a hukuncin da ya yanke, ya ce kotu na da hurumin gurfanar da Emefiele da wanda ake tuhuma, Henry Omoile.

Sai dai alkalin kotun ya yi fatali da tuhume-tuhume hudu daga cikin tuhume-tuhume 26 da EFCC ta shigar a kan su.

Hukumar EFCC ta gurfanar da Emefiele ne a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume 26, da suka shafi karkatar da kudaden da suka kai dala biliyan 4.5 ba bisa ka’ida ba da kuma Naira biliyan 2.8.

A ranar 12 ga Disamba, 2024, lauyan Emefiele, Mista Olalekan Ojo mai mukamin SAN, ya bayar da hujjar cewa kotun ba ta da hurumin sauraren karar a Legas.

Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta dakatar da Emefiele a matsayin gwamnan CBN a ranar 14 ga Yuni, 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp