Home General Ana fargabar mutuwar tarin Sojin Najeriya a wani sabon harin ISWAP

Ana fargabar mutuwar tarin Sojin Najeriya a wani sabon harin ISWAP

Wasu rahotanni daga jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya sun ce ƴan ta’adda sun sake farmakar ayarin Sojin ƙasar da ke kan hanyarsu ta laluben gawarwakin manoma 40 da ISWAP ta hallaka a garin Dumba na yankin Baga da ke ƙaramar hukumar Kukawa a jihar.

Wasu majiyoyi daga yankin sun tabbatar da cewa mayaƙan ISWAP ne suka ƙaddamar da harin kuma har kawo yanzu babu cikakkun alƙaluman sojojin da aka rasa a wannan farmaki.

Wata majiya daga ɓangaren ƴan sa kan ta bayyana cewa tun da farko adadi mai yawa na Sojin Najeriya tare da ƴan sakai 54 ciki har da mafarauta ne suka shiga dajin don laluben gawarwakin sai dai har zuwa yanzu ɗan sa kai 1 ne tal ya dawo cikin Baga a galabaice.

A cewar bayanai sun ce da farko sojojin sun so daƙile harin ƴan ta’addan amma kuma yawan makaman da mayaƙan ke ɗauke da shi ya tilasta musu ja da baya.

Rahotanni sun ce babu tabbacin Soji nawa suka mutu ko kuma nawa suka jikkata haka zalika a ɓangaren mayaƙan na sa kai lura da cewa hatta mutum guda da ya dawo cikin gari baya cikin hayyacinsa da zai iya bayar da labarin abin da ya faru.

Sai dai wata majiya daga ɓangaren Sojin Najeriya ta ce tuni wasu daga cikin dakarun na ta suka dawo sansaninsu da ke Baga.

A cewar majiyoyin Sojin sun birne 15 daga cikin manoman da ƴan ta’addam suka kashe sai sun haɗu da farmaki a lokacin da suka kai tsakiyar hanya a ƙoƙarinsu na isa Dumba, amma sun ci gaba da tafiya bana kawar da barazanar ƴan ta’addan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp