Home General An sace kayan wutar lantarki a birnin Abuja

An sace kayan wutar lantarki a birnin Abuja

Hukumar rarraba lantarki ta Najeriya (TCN) ta sanar da cewa wasu mutane sun ɓarnata tare da sace kayan wuta da ke samar da lantarki ga wasu sassa na Abuja, babban birnin ƙasar.

Sanarwar da hukumar ta fitar a jiya Juma’a ta ce “an lalata layin wutar lantarkinta na 132kV da wayoyin ƙarƙashin ƙasa waɗanda ke kai lantarki zuwa cikin ƙwaryar Abuja da unguwannin da ke kewaye, lamarin da ya kawo katsewar lantarki”.

Lamarin dai ya jefa unguwannin Abuja da dama cikin duhu, tare da haifar da wahalahalu ga al’umma.

Sanarwar, wadda ta samu sa hannun jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Ndidi Mbah, ta ce wayoyin su ne ke kai lantarki ga cibiyoyin rarraba lantarki na kamfanin AEDC domin samar da lantarki ga al’umma.

“Lamarin wanda ya faru a kusa da Millenium Park da ke Abuja, ya shafi fiye da kashi 60 cikin ɗari na lantarkin da ake samar wa birnin,” in ji sanarwar.

Bayanin ya tabbatar da cewa maɓarnatan sun sace wayoyin lantarki da sauran kayan wuta da dama.

Unguwannin da abin ya shafa sun haɗa da Maitama, da Wuse, da Jabi, da Life Camp, da Asokoro, da Utako da kuma Mabushi.

Hukumar ta TCN ta ce ta tura jami’anta domin yin gyara a inda aka sace kayan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp