Home General Dubu 55 muka sayi ko wacce akuya ba dubu 350 – Gwamnan...

Dubu 55 muka sayi ko wacce akuya ba dubu 350 – Gwamnan Kano

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ake yadawa cewa ta sayi kowacce akuya cikin awakin da zata rabawa matan karkarkara a wani bangare na yunkurin gwamnatin jihar na tallafa musu kan farashin naira dubu 350.

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Waiya, ne ya bayyana hakan ta cikin wani sakon murya da ya aike da manema labarai a yau Alhamis a birnin Kano.

Waiya ya ce an siyi Akuyoyi guda dubu 7158 kan kudi naira miliyan 451, inda za a raba wa mutane dubu 2386, sai Raguna guda 1975 kan kudi naira miliyan 351 da dudu 750 da za raba su ga mutane 987.

Haka zalika an siyi Shanu guda 1400 kan kudi naira biliyan 1 da miliyan 120 wadanda za a raba wa mutane 700, sai kuma kudin ciyarwa da magani da sauran hidinhimu da aka ware na naira miliyan 427 da dubu 958.

Kwamishinan ya kara da cewa jimullar kudin da aka ware sune naira Biliyan 2 da naira miliyan 350 sabanin abinda ake yada wa kan cewar kowacce akuya an siye ta kan naira dubu 350.

‘’’wannan shi ne abunda aka ware ko aka yi da su wato naira miliyan dubu 2 da naira miliyan 350 sabanin abinda mutane suke ta yamadidi da shi’’ Waiya.

Sai dai waiya ya yi zargin cewa an yada labarin da gangan dan a bata gwamnati har ya shawarci manema labarai su dinga bincike kafin su yada wani abu don kaucewa yada fitina a tsakanin al’umma.

‘’Wannan ba daidai ba ne yakamata al’umma su dinga jin tsoron Allah kan abubuwan da suke yi kuma su fahimci cewa ya madidi da abinda yake na zance na karya ba daidai ba ne’’ Waiya’’.

A karshe Waiya ya ce duk wanda ya duba jawabin gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana dukkan adadin kudaden da aka yi daki-daki.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp