Home General Martanin gwamnatin jihar Zamfara kan rahoton UNICEF na tamowa

Martanin gwamnatin jihar Zamfara kan rahoton UNICEF na tamowa

Hukumomi a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya sun mayar da martani game da bayanin da asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya ya yi cewa akwai yara dubu 250 da ke fama da matsananciyar yunwa daga cikin yara miliyan daya da dubu dari biyu da aka yi nazari a kansu a jihar.

Gwamnatin jihar ta ce lokacin da ta karbi mulkin jihar ta tarar da harkokin kula da lafiya ba kamar yadda ta yi tsammani ba, amma a cewar kwamishinan yada labaran jihar, Mahmud Muhammad Dantawasa sun dauki matakai dai-dai gwargwado.

“Yanzu haka gwamnati na gyara asibitocin matakin farko da suke a karkara guda 62 wadanda yawancinsu angama gyaransu kuma yanzu haka ana raba maganin tamowa a asibitin.”

Gwamnatin ta kuma yi kira ga iyayen yara da su riƙa zuwa wadannan asibitoci domin karɓar maganin tamowar kyauta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp