Home AFIRKA ECOWAS ta tabbatar da ficewar Nijar, Burkina Faso da kuma Mali a...

ECOWAS ta tabbatar da ficewar Nijar, Burkina Faso da kuma Mali a hukumance

Kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen Yammacin Afirka ta ECOWAS ta tabbatar da ficewar kasashen Burkina Faso, Mali da kuma Nijar a hukumance

Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da ECOWAS din ta fitar, tana mai cewa har yanzu kofa a bude take ga wadannan kasashe, a duk lokacin da suka sauya shawarar sake koma wa.

A cikin sanarwar, ECOWAS ta ce za a ci gaba da mutunta fasfon jama’ar wadannan kasashe uku da ke dauke da tambarin ECOWAS, hadi da katinsu na shaidar dan kasa.

Haka zalika kungiyar ta ce za a ci gaba da kallon wadannan kasashe tamkar mambobinta, har ma ta bayyana a cikin sanarwar cewa, harkokin kasuwanci tsakanin kasashe mambobin ECOWAS da kuma kasashen Nijar, Burkina Faso da kuma Mali zasu ci gaba da tafiya kamar yadda suke a baya.

Sanarwar ta kuma bukaci kasashen kungiyar, da su ci gaba da bawa jama’ar kasashen uku damar shiga kasashensu ba tare da takardar izinin shiga ba, da kuma zama, har sai baba ta gani.

Kungiyar ta ce an fitar da wannan sanarwa ne, domin kaucewa haifar da zaman tankiya ko kuma dardar tsakanin jama’ar wadannan kasashe uku, musamman ‘yan kasuwa, da kuma kwantar musu da hankula.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp