Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka manyan “ƴanta’adda” a jihohin Zamfara da Sokoto

Sojojin Nijeriya sun hallaka manyan “ƴanta’adda” a jihohin Zamfara da Sokoto

Nigerian Army

Rundunar Fansan yamma da ke yaƙi da ƴan bindiga a jihohin Zamfara da Sokoto ta ce ta samu gagarumar nasarar karya lagon “yanta’adda” daga ranar 1 zuwa 10 ga watan Fabrairun 2025.

Rundunar wadda ta shaida hakan a wata sanarwa da ta fitar ta hannun mai magana da yawunta, Laftanar Kanar Abubakar Abdullahi, ta ce aikin da rundunar ta yi ya ci galaba kan “ƴanta’adda” da suka haɗa da manyan ƴanbindiga.

A yayin aikin rundunar, dakarun soji sun yi nasarar kashe gomman “ƴanta’adda” da suka haɗa da manyansu irin su Kachalla na Faransa da Dogon Bakkwalo da Auta Gobaje da Dan Mai Dutsi.

Sanarwar ta ce yawancin ƴanbindigar na addabar al’ummar yankunan da ke ƙananan hukumomin Shinkafi da Zurmi da ke jihar Zamfara da kuma ƙaramar hukumar Isa ta jihar Sokoto

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp