Home General Gwamnan Kano ya haramta sanya dalibai aikin wahala a makarantu

Gwamnan Kano ya haramta sanya dalibai aikin wahala a makarantu

Gwamnan jihar Kano Eng. Abba Kabir Yusuf ya gargadi malamai da su daina tilastawa dalibai yin aikace-aikace masu wahala a ciki ko a wajen makaranta

Haramcin na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sunusi Bature Dawakin-Tofa, ya fitar aka raba manema labarai a jihar kano.

Gwamnan ya jaddada cewa makarantu wuraren karatu ne na koyar da ilimi da tarbiyya, ba wuraren yin aikin wahala ba.

Yayin wata ziyarar bazata da ya ka makarantar koyon harshen larabci (School for Arabic Studies) Kano, gwamnan ya tarar da wasu dalibai suna tonon ramin bututun bayan gida.

Inda cikin fushi, gwamnan ya tambayi shugaban makarantar dalilin da ya sa aka ba dalibai irin wannan aiki.

Shugaban makarantar ya shaidawa gwamna cewa aikin an ba su ne bayan an tashi daga makaranta.

Sai dai nan take gwamnan ya bayar da umarnin dakatar da yaran da aka sa aikin, ya kuma tabbatar wa shugabannin makarantar cewa gwamnatinsa za ta gyara dukkan gine-ginen da suka lalace, har da masallacin da ke cikin makarantar.

Haka kuma, ya bada umarni cewa duk wata bukata ta gyaran makaranta a mikata ga Ma’aikatar Ilimi ko ofishinsa domin aiwatarwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp