Home General Dakarun Najeriya sun kashe ‘yan ta’adda 82 tare da kama 198 a...

Dakarun Najeriya sun kashe ‘yan ta’adda 82 tare da kama 198 a mako guda

Shelkwatar tsaron Najeriya ta ce dakarunta sun kashe ƴan ta’adda 82  tare da kama guda 198, suka kuma ceto mutane 93 da aka yi garkuwa da su a cikin mako guda da ya wuce a sassan ƙasar.

Daraktan yaɗa labarai na ma’aikatar, Manjo Janar Markus Kangye,  ne ya bayyana haka a Abuja,  a yayin da ya ke yi wa manema labarai bitar nasarorin  da dakarun ƙasar suka samu.

Kangye  yace dakarun sun kuma ƙwace ɗimbim makamai da ababen hawa a daga ƴan ta’addan a samamen da suka yi daga ranar 14 zuwa 21 ga watan Fabrairu.

Ya ce dakarun sun ƙwace bindigogi da suka haɗa da AK47 guda 46, bindigogin da aka ƙera a gida guda 18, sai bindigogin zari-ruga guda 19 da harshasai sama 1,200.

Kakakin ma’aikatar tsaron ya ƙara da cewa ƴan ta’addda 41 sun miƙa wuya ga dakarun rundunar Operation HADIN KAI a yankin arewa maso gabashin ƙasar, kuma daga cikin su akwai manya baligai 41, sai yara 19.

Janar Kangye ya ƙara da cewa dakarun na Najeriya sun kama masu satar mai a yankin Kudu maso Kudancin ƙasar, sun kuma daƙile satar da kiyasta darajarta ta kai naira 587.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp