Home General Rundunar ‘yan sandan Kano ta magantu Kan rufe titin gidan Gwamnatin Kano

Rundunar ‘yan sandan Kano ta magantu Kan rufe titin gidan Gwamnatin Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayyana cewa ta rufe wasu hanyoyin ne da suke dangana mutane da gidan sarki na Nasarawa dake kan titin zuwa gidan gwamnati saboda bayanan sirri da suka samu na kokarin kawo hargitsi a jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na Rundunar yan sandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar ranar laraba.

Ya ce “A sakamakon wadannan matakan da aka dauka, an kama wasu mutane 17 da ake zargi da aikata laifuka, kuma ana ci gaba da bincike. Rundunar zata tabbatar ta gurfanar da wadanda ake zargi da aikata wannan tashin hankali a gaban kuliya.

Rundunar ta gargadin daidaikun mutane da kungiyoyi game da yin duk wani nau’i na taro, jerin gwano, bisa ka’ida ba. Kaucewa Wannan gargadi zai iya sawa jami’an tsaro su dauki mataki.

Kiyawa ya yi kira ga jama’a da su sanya ido tare da kai rahoto ga jami’an tsaro na duk wani abu da ba su aminta da shi ba, haka kuma Rundunar ta yaba da hadin kai da goyon bayan mutanen jihar Kano ke ba ta a kokarinsu na wanzar da zaman lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp