Home General NMDPRA ta sake bayar da lasisin buɗe sabbin matatun man fetur a...

NMDPRA ta sake bayar da lasisin buɗe sabbin matatun man fetur a Najeriya.

Hukumar Kula da Albarkatun Mai Na Ƙasa (NMDPRA) ta bayar da lasisin buɗe sabbin matatun man fetur a Najeriya.

Hukumar ta ce ta ba wasu kamfanoni guda uku lasisin ne domin buɗe matatun a jihohin Abia da Delta da Edo.

Shafin intanet na tashar Channels ne ya kalato labarin daga shafin X na NMDPRA, inda ya ƙara da cewa za a buɗe Matatar Eghudu wadda za ta iya tace ganga 100,000 a kullum a jihar Edo.

Za kuma da Matatar MB wadda za ta riƙa tace ganga 30,000 a kullum a jihar Delta, sai Matatar HIS wadda ita kuma za ta riƙa tace ganga 10,000 a kullum a jihar Abia, kamar yadda sanarwar, wadda shugaban hukumar, Farouk Ahmed ya bayyana ta nuna.

Idan aka kammala su, matatun guda uku za su riƙa tace ganga 140,000 ke nan a kullum.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar KatsinaZaben 2027: NDC ta Tsayar da Ɗan Kwankwaso Mataimakin ɗan Takarar Gwamnan KanoKotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja
X whatsapp