Home General NMDPRA ta sake bayar da lasisin buɗe sabbin matatun man fetur a...

NMDPRA ta sake bayar da lasisin buɗe sabbin matatun man fetur a Najeriya.

Hukumar Kula da Albarkatun Mai Na Ƙasa (NMDPRA) ta bayar da lasisin buɗe sabbin matatun man fetur a Najeriya.

Hukumar ta ce ta ba wasu kamfanoni guda uku lasisin ne domin buɗe matatun a jihohin Abia da Delta da Edo.

Shafin intanet na tashar Channels ne ya kalato labarin daga shafin X na NMDPRA, inda ya ƙara da cewa za a buɗe Matatar Eghudu wadda za ta iya tace ganga 100,000 a kullum a jihar Edo.

Za kuma da Matatar MB wadda za ta riƙa tace ganga 30,000 a kullum a jihar Delta, sai Matatar HIS wadda ita kuma za ta riƙa tace ganga 10,000 a kullum a jihar Abia, kamar yadda sanarwar, wadda shugaban hukumar, Farouk Ahmed ya bayyana ta nuna.

Idan aka kammala su, matatun guda uku za su riƙa tace ganga 140,000 ke nan a kullum.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp