Home General Majalisar wakilan Nijeriya zata dauki tsahon wunin yau tana tsefe dokar haraji

Majalisar wakilan Nijeriya zata dauki tsahon wunin yau tana tsefe dokar haraji

Majalisar wakilan Nijeriya ta ce a yau zata fara tsefe rahoton kwamitin sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin dokar haraji.

Kakakin Majalisar, Hon. Tajudeen Abbas ne ya bayyana haka a zaman majalisar na ranar Laraba.

Hon Tajudeen ya ce majalisar za ta ɗauki tsawon wunin yau, Alhamis tana nazari da muhawara kan sassan ƙudirin dokar daban-daban.

Kakakin majalisar ya kuma yi kira ga duka mambobin majalisar su halarci zaman domin bayar da tasu gundunmawa kan rahoton kwamitin sauraron ra’ayin jama’ar.

Tuni dai kwamitin sauraron ra’ayin jama’ar – ƙarƙashin jagorancin shugaban kwamitin kuɗi na majalisar, Hon James Abiodun Faleke – ya kammala sauraron jin ra’ayin jama’a inda ya miƙa rahoton nasa a gaban majalisar a ranar Talata

A watan Oktoban bara ne shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya gabatar da ƙudurori huɗu da suka shafi haraji a gaban majalisun dokokin ƙasar, domin amincewa da su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp