Home General Fubara ya rubutawa Majalisar Jihar Rivers Wasika

Fubara ya rubutawa Majalisar Jihar Rivers Wasika

Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya sake rubuta wa majalisar dokokin jihar wasiƙar sanar da ƴanmajalisar aniyarsa ta sake gabatar da kasafin kuɗin jihar na shekarar 2025, domin neman amincewarsu.

Cikin wasiƙar da gwamnan ya aike wa kakakin majalisar dokokin jihar, Martin Amaewhule ranar Alhamis ya ce yana son gabatar da kasafin a gaban ƴanmajalisar a ranar Laraba 19 ga watan Maris, ko a wata rana cikin watan Maris da majalisar ke ganin zai fi dacewa.

Fubara ya ce matakin biyayya ce ga hukuncin Kotun Ƙolin ƙasar, da kuma buƙatar da ƴanmajalisar suka yi masa na sake gabatar musu kasafin kuɗin jihar.

A cikin wasiƙar gwamnan ya tuna wa kakakin majalisar zuwansa zauren majalisar a ranar Laraba da nufin gabatar da kasafin, amma sai aka kulle ƙofar aka hana shi shiga tare da tawagarsa.

“Za ka iya tuna ziyarar da kawo majalisar a ranar Laraba 12 ga watan Maris domin gabatar da kasafin, domin biyayya ga hukuncin Kotun Ƙoli, amma ba a ba ni damar shiga zauren majalisar ba”, kamar yadda wani ɓangare na wasiƙar ya nuna.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp