Home General An samu fashewar ɗaya daga cikin manyan layin bututu man Najeriya

An samu fashewar ɗaya daga cikin manyan layin bututu man Najeriya

An samu wata fashewa a ɗaya daga cikin manyan layin bututu man Najeriya, da ke garin Bodo na ƙaramar hukumar Gokana da ke jihar Rivers.

A cikin daren jiya Litinin ne dai aka samu fashewar a bututun TNP, da Najeriya ke amfani da shi wajen tura mai tashar mai ta Bonny da ke jihar ta Rivers.

Har zuwa safiyar Talatar nan, ɓangaren da aka samu fashewar na ci da wuta, lamarin da ya sanya bakin haraƙi turnuke sararin samaniya.

Kawo yanzu dai hukumomin ƙasar basu tantance abinda ya haifar da fashewar ba, duk da dai akwai barazanar da tsageran yankin suka yi a kwanan nan na kai wa cibiyoyin mai hari, sakamakon yadda a baya-bayan nan gwamnatin ƙasar taƙi tura wa jihar kuɗaɗenta na wata-wata, bisa rikicin siyasar jihar da ke faruwa tsakanin ɓangaren zartarwa da na dokoki.

Itama dai kakakin rundunar ƴan sandan jihar Grace Iringe-Koko, ta ce basu kammala tattara baranai ba don sanin haƙiƙanin abinda ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp