Home General An samu fashewar ɗaya daga cikin manyan layin bututu man Najeriya

An samu fashewar ɗaya daga cikin manyan layin bututu man Najeriya

An samu wata fashewa a ɗaya daga cikin manyan layin bututu man Najeriya, da ke garin Bodo na ƙaramar hukumar Gokana da ke jihar Rivers.

A cikin daren jiya Litinin ne dai aka samu fashewar a bututun TNP, da Najeriya ke amfani da shi wajen tura mai tashar mai ta Bonny da ke jihar ta Rivers.

Har zuwa safiyar Talatar nan, ɓangaren da aka samu fashewar na ci da wuta, lamarin da ya sanya bakin haraƙi turnuke sararin samaniya.

Kawo yanzu dai hukumomin ƙasar basu tantance abinda ya haifar da fashewar ba, duk da dai akwai barazanar da tsageran yankin suka yi a kwanan nan na kai wa cibiyoyin mai hari, sakamakon yadda a baya-bayan nan gwamnatin ƙasar taƙi tura wa jihar kuɗaɗenta na wata-wata, bisa rikicin siyasar jihar da ke faruwa tsakanin ɓangaren zartarwa da na dokoki.

Itama dai kakakin rundunar ƴan sandan jihar Grace Iringe-Koko, ta ce basu kammala tattara baranai ba don sanin haƙiƙanin abinda ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp