Home General NLC ta bukaci Tinubu ya gaggauta Mayar da Fubara

NLC ta bukaci Tinubu ya gaggauta Mayar da Fubara

Kungiyoyin kwadagon Najeriya NLC da TUC sun yi kakkausan Allah wadai da abin da suka bayyana a matsayin saba doka da shugaba Tinubu ya yi, wajen kafa dokar ta-baci da dakatar da gwamnan jihar Siminilayi Fubara, da mataimakiyarsa, da yan majalisar dokokin jihar Rivers.

Kungiyoyin sun ce matakin ya saba wa tanadin sashe na biyu, da sashe na 305 na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 wanda aka yi wa kwaskwarima, kuma ya zama cin zarafi ga ikon zartarwa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kungiyoyin suka fitar ranar Larabar nan,kwana guda bayan shugaba Tinubu ya sanar da matakin na sa, da ya haifar da ce-ce-ku-ce a fadin kasar.

Sanarwar ta bukaci shugaban kasar ya gaggauta janye sanarwar da ya bayar, da ka iya dora kasar a kan tubalin sabawa doka a nan gaba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp