Home General Sojojin Nijeriya sun ceto mutane Sama da dari a Jihohi Katsina da...

Sojojin Nijeriya sun ceto mutane Sama da dari a Jihohi Katsina da Zamfara

Sojojin Najeriya ƙarƙashin rundunar Operation Fansan Yamma sun ce sun ceto mutum 101 da aka yi garkuwa da su a ƙananan hukumomin Ƙanƙara da ke jihar Katsina da kuma Shinkafi a jihar Zamfara.

Shugaban sashen yaɗa labarai na rundunar, Laftanar-kanar Abubakar Abdullahi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Laraba.

Sanarwar ta ce rundunar ta samu nasarar ce a wani samame da ta ƙaddamar kan dabobin ƴan fashin daji a ranakun 17 da 18 ga wannan wata na Maris.

Sanarwar ta ƙara da cewa a lokacin samamen an kashe ƴan fashi 10 a fafatawar da aka yi tsakanin dakaru da ƴan fashin a yankin Faru na ƙaramar hukumar Maradun.

Haka nan sanarwar ta ce an fara samamen ne daga yankin Tudun Pauwa na ƙaramar hukumar Ƙanƙara a jihar Katsina, inda aka kashe ƴan fashin daji uku tare da ceto mutum 83 da aka yi garkuwa da su.

Sannan bayan tattara bayanan sirri, rundunar ta kai farmaki a Bagabuzu na yankin Faru a jihar Zamfara, inda ta kashe ƴan fashi 7 da ƙwato wasu kayayyaki, ciki har da babur.

Zamfara da Katsina, jihohi ne da ke fama da matsalar ayyukan ƴan fashin daji wadanda ke kai farmaki a ƙauyuka, suna kisa da kuma garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

Dukkanin jihohin biyu sun kafa rundunonin sintiri wadanda ke taimaka wa dakarun sojin Najeriya wajen yaƙi da matsalar, wadda aka shafe shekara da shekaru ana fama da ita.

Hare-haren ƴan bindigan sun haifar da asarar rayuka da durƙusar da ayyukan tattalin arziƙi a yankunan, tare da tarwatsa mutane daga muhallansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp