Home General Gwamna Abba ya nada Aramposu mukami

Gwamna Abba ya nada Aramposu mukami

Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusif, ya yi sabbin naɗe-naɗe tare da ɗaga likkafar wasu mutane a ƙunshin gwamnatinsa.

Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar a daren Laraba, inda ya ce canje-canjen zai ƙara gogar da shugabannin gobe masu tasowa da kuma ƙara inganta kyakkyawan jagorancin gwamnatin jihar.

Sabbin naɗe-naɗe sune kamar haka;

1- Akitek Hauwa Hassan Tudun Wada – shugabar hukumar kula da tsara birane ta jihar kano (KNUPDA)

2- Mustapha Muhammad – Sakataren yaɗa Labaran Gwamnan kuma mataimakin kakakin Gwamnan.

3- Auwal Lawan Aramposu – Mataimakin Shugaban hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Kano (KAROTA).

4- Dakta Tukur Ɗaiyabu Minjibir – Mai bawa Gwamnan shawara kan harkokin Noma da Kiwo (Agriculture).

Haka kuma gwamnan ya amince da ɗaga likkafar wasu ƙusoshin gwamnatin guda biyu waɗanda suka haɗar da;

1- Hajiya Zulaihat Yusuf Aji – Mataimakiyar Shugaban gidan rediyon Kano, wanda a baya ta kasance babbar mai bawa Gwamna Shawara kan yaɗa labarai.

2- Injiniya Abduljabbar Nanono – Mataimakin Shugaban hukumar samar da wutar lantarki ta jihar kano KHEDCO, wanda a baya shine Mashawarcin Gwamnan akan sabbin dabarun makamashi.

A ƙarshe gwamnan ya taya su murnar muƙaman da suka samu, har ma ya buƙaci suyi aiki tuƙuru wajen sauke nauyin da aka ɗora musu domin samun nasarar gwamnatin na ciyar da jihar gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp