Home General M23 ta sake ƙwace wani yanki a Congo bayan watsi da kiran...

M23 ta sake ƙwace wani yanki a Congo bayan watsi da kiran tsagaita wuta

Shugaban ‘yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda a gabashin Congo ya yi watsi da tayin da Kinshasa da Kigali suka yi na tsagaita wuta cikin gaggawa, yayin da dakarunsa suka shiga cikin yankunan gabashin Congo tare da sake ƙwace garin Walikale mai muhimmanci.

Bayan karɓe ikon wasu manyan birane guda biyu a gabashin ƙasar ta Congo, birnin na Walikale dake da tazarar kilomita 125 daga babban birnin ƙasar Kinshasa wanda ke ɗaya daga cikin masu tarin arzikin ma’adanai da ya shiga kwamar ƴan tawayen na M23.

Garin mai yawan al’umma 15,000 ya faɗa ƙarƙashin ikon ƴan tawayen ne bayan wani ƙazamin faɗa da ya ɓarke a tsakaninsu da dakarun sojin ƙasar ta Jamhuriyyar Congo.

Faɗan, wanda ya samo asali daga kisan kiyashi da aka yi a kasar Rwanda a shekarar 1994 da kuma gogayya kan mallakar arzikin albarkatun ƙasa, shi ne mafi muni a gabashin Congo tun bayan yakin shekarar 1998 zuwa 2003 wanda ya yi sanadin mutuwar miliyoyin mutane.

A yayin da masana suka bayyana cewa wannan yaƙin da ƙasashen Congo da Rwanda da kuma Burundi suka tsunduma cikinsa a wannan shekara, ya munana bisa yadda yake ƙoƙarin bazuwa yankin baki ɗayansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp