Home General ‘Ya Ta’adda sun kashe masallata 44 a Nijar

‘Ya Ta’adda sun kashe masallata 44 a Nijar

Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun ayyana makoki kwana uku bayan wasu ‘yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 44 yayin da suke sallar Juma’a.

Rahotonni sun ce harin ya jikkata mutum 13, huɗu daga cikinsu na cikin mawuyacin hali a harin da aka kai garin Kokorou da ke kan iyakar Nijar da Mali da Burkina Faso.

Wata sanarwa da Ministan Harkokin Cikin Gida Mohamed Toumba ya fitar ta ce maharan da ke biyayya ga ƙungiyar Islamic State wato Islamic State in the Greater Sahara (ISGS) ne suka kai harin a ranar Asabar.

“Da misalin ƙarfe 2:00 na rana, daidai lokacin da Musulmai ke yin sallar Juma’a maharan suka kewaye masallacin domin aikata kashe-kashen da ba a saba gani ba,” in ji ministan.

Kazalika, sun cinna wa “kasuwa da gidajen mutane wuta,” kamar yadda ya bayyana.

Kwana biyu kafin wannan hari rundunar sojin Nijar ta ce ta kashe mambobin ISGS 45.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp