Home General An saka dokar taƙaice zirga-zirga a mazaɓar Sanata Natasha

An saka dokar taƙaice zirga-zirga a mazaɓar Sanata Natasha

Shugaban ƙaramar hukumar Okehi da ke jihar Kogi, Amoka Monday, ya ayyana dokar taƙaita zirga-zirga a yankin ƙaramar hukumar sakamakon fargabar ɓarkewar rikici saboda haramta tarukan siyasa da gwamnan jihar ya yi a ranar Litinin.

A watan sanarwa da shugaban ƙaramar hukumar ya sanya wa hannu wadda jaridar Punch ta rawaito, Amoka Monday ya ce dokar taƙaita zirga-zirgar dole ce domin samar da zaman lafiya a ƙaramar hukumar.

Wannan dai ya biyo bayan sanarwar da Sanata Natasha ta fitar tana mai nanata cewa za ta yi gangamin siyasa a ƙaramar hukumar duk da hanin da rundunar ƴansandan jihar ta yi mata.

A ranar Litinin ne gwamna Ododo ya haramta dukkan wani taron siyasa a jihar.

Magoya bayan Sanata Natasha dai sun ce za su yi wannan gangami ne domin nuna goyon baya ga wakiliyar tasu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp