Home General An bayyana lokacin Janaídar Wamban Kano

An bayyana lokacin Janaídar Wamban Kano

Masarautar Kano ta yi rashin guda daga cikin manyan jagorin da su ka yi shura wurin al,amuran mulki da jagoranci shekaru masu tsawo, Galadiman Kano Alhaji Abbas Sanusi, dan sarkin Kano Abbas Abdullahi Bayero.

Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi ya rasu ya na da shekaru 92 a duniya, a ranar talata da dare.

Ya kasance jigogin cikin wadanda da suka shahara a Masarautar Kano. A zamanin marigayi Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero, shi ne Wamban Kano, Kuma Babban Dan majalisar Sarki.

Shugaban Jam’iyyar APC a jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas da Dan uwansa, Alhaji Kabiru Abbas su ne su ka tabbatar da rasuwar mahaifin na su bayan jinya da ya yi ta tsawon lokaci.

Rasuwar marigayi Galadiman Kano rashi ne ga al’ummar Arewacin Nijeriya ba ma iya masarautar kano ba kadai.

Ya rike mukamai daban-daban, karkashin Sarkin Kano Ado Bayero, wanda ya kasance a karagar masarautar daga shekarar 1963 zuwa 2014.

Ya rasu ya bar mata da ‘yaya 35, daga cikinsu akwai shugaban jami’iyyar APC na jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas.

Za a gudanar da jana’izarsa a  fadar masarautar Kano, dake kofar kudu da karfe 9 na safiyar ranar larabar nan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp