Mai shari’a Binta Nyako na babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da shugaban majalisar dattijai, Godswill Akpabio da kuma wasu mutum uku daga tattauana batun shari’arsu da manema labarai.
Mai shai’a Nyako ta yanke hukuncin ne ranar Juma’a bayan ƙorafin da lauyan da ke kare Akpabio ya yi cewa Natasha na bin daga wannan gidan talabijin zuwa wancan, don tattaunawa da manema labarai kan shari’arsu, duk da cewa batun yana gaban kotu.
Kotun ta ce daga yanzu babu ɓangaren da zai tattauna da manema labarai dangane da batun.
Nyako ta kuma haramtawa Akpabio da Natasha da kuma lauyoyinsu daga yaɗa zaman shari’ar kai-tsaye a shafukan sada zumunta.











