Home General Mutane da dama ne suka mutu a wani fada a Sudan ta...

Mutane da dama ne suka mutu a wani fada a Sudan ta Kudu

Akalla mutane 30 ne aka kashe a fadan da aka yi a wani gari da ke arewacin Sudan ta Kudu wanda wasu gungun matasa ɗauke da makamai suka mamaye na wani dan lokaci bayan wani farmakin da suka kai na shanu, kamar yadda wani jami’in yankin ya sanar a jiya Alhamis.

Lamarin ya faru a yankin arewacin Ruweng a farkon mako lokacin da wasu matasa dauke da makamai suka sace raguna kafin jami’an tsaro su fatattake su, in ji Simon Chol Mialith, ministan yada labaran yankin.

Washegari, kamar yadda ya shaida wa AFP, kungiyar matasan ta dawo da yawa inda suka kai hari a garin Abiemnom.

Ministan ya kara da cewa, “matasa da jami’an tsaro sun yi kokarin kare birnin amma matasa dauke da makamai suka mamaye su.

A ranar Larabar da ta gabata ce Dakarun tsaron Sudan ta Kudu (SSPDF) suka fatattaki ‘yan kungiyar da ke dauke da makamai tare da samun kwanciyar hankali, in ji Mialith. “Akwai matattu talatin da kuma jikkata kusan arba’in,” ​​in ji shi, ba tare da yin karin bayani ba.

Kafofin yada labaran cikin gida sun ruwaito cewa wasu daga cikin wadanda aka kashe na kungiyar ne, amma kamfanin dillancin labaran AFP ya kasa tabbatar da wannan labarin.

Rikici tsakanin makiyaya da al’ummomin da ba sa zaman kashe wando dai ya zama ruwan dare a Sudan ta Kudu, sai dai wadannan al’amura na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin siyasa ya tsananta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp