Home General Sojojin Najeriya sun hallaka ƙasurgumin ɗanbindiga Gwaska da wasu guda 100

Sojojin Najeriya sun hallaka ƙasurgumin ɗanbindiga Gwaska da wasu guda 100

Hukumomi a Najeriya sun ce jami’an tsaron ƙasar sun halaka ƴanbindiga 100 ciki har da gawurtaccen ɗanbindiga, Gwaska a jihar Katsina da ke Arewa Maso Yammacin Ƙasar.

Hadin gwiwar jami’an tsaron kasar ne suka ƙaddamar da harin a ranar Juma’a wanda ya yi sanadin kisan Gwaska – wanda ya kasance mataimakin shahararren ɗanbindiga Malan, shugaban ISWAP a yankin Arewa Maso Yamma.

Bayanai sun nuna cewa Gwaska Dankarami ya jima yana ɓuya a dajin Munumu da ke jihar Katsina.

Rahotonni sun ce sojojin sun lalata maɓoyar ƴanbindigar da dama a sassan jihar a lokacin harin, tare da ƙwato da kuma lalata wasu manyan bindigogi masu jigida da waɗanda aka ƙera a cikin gida.

Harin na zuwa ne bayan da a farkon mako ƴanbindigar suka yi garkuwa da mutum 43 mazauna ƙauyukan Maigora da ke yankin ƙaramar hukumar Dandume

Kwamishinan al’amuran cikin gida na jihar Katsina, Nasir Mu’azu ya bayyana matakin da wata gagarumar nasara a yaƙi da ƴanbindiga ake yi a jihar.

“Abin farin ciki ne ga jihar, domin wannan nasara ta taimaka wajen wargaza hadakar ƴanbindigar da ke addamar garuruwa da ƙauyukan yankunan ƙananan hukumomin Faskari da Kankara da Bakori da Malumfashi da kuma Kafur,” in ji Kwamishinan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp