Home General PDP ta ce ba za ta yi haɗaka da kowa ba

PDP ta ce ba za ta yi haɗaka da kowa ba

Gwamnonin babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya sun nisanta kansu da yunƙurin haɗaka tsakanin jam’iyyarsu da wasu jam’iyyun siyasa.

Ƙungiyar gwamnonin ƙarƙashin gwamnan Bauchi Bala Mohammed ta ce ba za ta haɗe da wata jam’iyya ba da nufin tunkarar zaɓen 2027.

“Ba za mu shiga wata haɗaka ba da kowa da nufin tunkarar zaɓen 2027,” kamar yadda ƙungiyar gwamnonin PDP ta bayyana a sanarwar da ta fitar bayan taron da suka gudanar a Ibadan jihar Oyo.

Wannan dai ya ci karo da iƙirarin tsohon ɗantakarar jam’iyyar kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar a kwanakin baya inda ya ce suna yunƙurin ƙulla haɗaka da wasu jam’iyyu.

Sanarwar gwamnonin PDP ya nuna akwai saɓanin ra’ayi tsakanin ɓangarensu da na Atiku Abubakar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp