Home General PDP ta ce ba za ta yi haɗaka da kowa ba

PDP ta ce ba za ta yi haɗaka da kowa ba

Gwamnonin babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya sun nisanta kansu da yunƙurin haɗaka tsakanin jam’iyyarsu da wasu jam’iyyun siyasa.

Ƙungiyar gwamnonin ƙarƙashin gwamnan Bauchi Bala Mohammed ta ce ba za ta haɗe da wata jam’iyya ba da nufin tunkarar zaɓen 2027.

“Ba za mu shiga wata haɗaka ba da kowa da nufin tunkarar zaɓen 2027,” kamar yadda ƙungiyar gwamnonin PDP ta bayyana a sanarwar da ta fitar bayan taron da suka gudanar a Ibadan jihar Oyo.

Wannan dai ya ci karo da iƙirarin tsohon ɗantakarar jam’iyyar kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar a kwanakin baya inda ya ce suna yunƙurin ƙulla haɗaka da wasu jam’iyyu.

Sanarwar gwamnonin PDP ya nuna akwai saɓanin ra’ayi tsakanin ɓangarensu da na Atiku Abubakar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp