Home Bincike Bincike: Shin da gaske ne masu zanga-zanga sun yi wa fadar sarkin...

Bincike: Shin da gaske ne masu zanga-zanga sun yi wa fadar sarkin Musulmi bisa bukatar Obi ko kuma a chanja Gwamnati?

Wani faifen Bidiyo da yayi ta yawo a kafafen internet da kafafen sada zumunta, musamman manhajar WhatsApp da shafin Facebook, wanda ta nuna wasu tarin mutane masu zanga-zanga sun yi wa fadar sarkin musulmi da ke sokoto tsinke in da suke bukatar sauyin gwamnatin idan wakilan gwamnatin tarayya sun kai ziyara jihar.

An rubuta cewa: “Sokoto a ya! Yadda ma su zanga-zanga suka taro a fadar Sarkin Musulmi, suna ihun “ ba ma Tinubu…. Sai Obi ko kuma Sojoji su karbi kasar.”

To amma, tawagar binciken sahihancin labarai ta PRNigeria ta bi diddigin asalin bidiyon da ake ikirari a kai, wadda aka wallafa a shafukan sada zumuntar da suka hadar da Facebook, bayan da karamin minstan tsaron Nijeriya Bello Matawalle ya jagorancin tawagar manyan sojoji zuwa Sokoto, domin duba ayyukan sojojin na kawar da matsalar rashin tsaro da ta addabi shiyyar Arewa maso yammacin Nijeriya.

https://www.premiumtimesng.com/regional/nwest/731118-matawalle-security-chiefs-arrive-in-sokoto-following-tinubus-order.html

haka kuma, wani bincike da aka fadada ya tabbatar da cewa bidiyon tsoho ne da aka dauka lokacin zanga –zangar ‘EndBadGovernance’, wadda ta gudana a watan Agustan 2024, akalla wata guda bayan ikirarin.

Zanga-zangar #EndBadGovernance, wadda aka fi sani da  #EndbadGovernanceInNigeria ta kunshi jerin zanga-zangar da babu wadanda suka shirya ta wadanda suka gudana a mabanbanta wurare a fadin Nijeriya da ka gudanar a 1 ga watan Agustan 2024 zuwa 10 ga watan. Wannan zanga-zanga ta faru ne sakamakon tsadar kayan masarufi a fadin kasar abin da ya haifar da tsadar rayuwa da wahalhalun rayuwa ga al’ummar kasar.

KAMMALAWA: binciken da jaridar PRNigeria ta gudanar ya tabbatar da wannan bidiyon da aka yada aka ce masu zanga-zanga ne a fadar sarkin musulmi da ke Sokoto lokacin da tawagar karamin ministan Tsaron Nijeriya da shuwagabannin tsaron kasar suka ziyarci fadar, gaskiya tsohon bidiyo ne na zanga-zangar EndBadGovernance da aka gudanar a watan Agustan 2024.

Don haka,  PRNigeria ta yanke hukuncin kan ikirarin da ake da ke cewa masu zanga-zanga a fadar mai Alfarma sakin musulmi da ke jihar Sokoto, da ke nuna goyon bayan Peter Obi ko sauya gwamnati labarin karya ne.

By PRNigeria

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp