Home Labarai Barau ya nada shugaban kungiyar zago akida na Kano mukami

Barau ya nada shugaban kungiyar zago akida na Kano mukami

Mataimakin shugaban majalisar dattijan Nijeriya sanata BarauIi. Jibril Maliya ya nada shugaban kungiyar zago akida na jihar Kano Muktar B.A. Gwammaja matsayin maitaimaka masa na musamman.

Wannan na cikin wata takarda da ta fito daga ofishin sanatan mai dauke da sa hannun Mai taimakawa sanatan ta musamman kan harkokin gudanarwa Ngozi Nkemdirim (Mrs) a madadin shugaban ma’aikatan ofishin mataimakin shugaban majalisar wakilan.

Takardar ta ce “Cikin girmamawa ina mai sanarwa da kai cewa an nada ka matsayin mai taimakawa na musamman ga mataimakin shugaban majalisar Dattijan Sanata Barau I. Jibril. Nadin zai fara aiki ne a ranar 1 ga watan Afirilun 2025, har zuwa watan Mayun 2027.”

Kafin nada shi mukamin ya kasance na hannun dama kuma Kuma mataimaki na musamman ga marigayi Amb A.Ahmad Haruna zago akan harkokin yada labarai da aiyuka na musamman, wanda daga bisani ya zama shugaban kungiyar zago akida ta jihar Kano.

Daga bisani sanarwa ta taya Mukhtar Ali (Muktar B.A.A) murna tare da yi masa fatan Alkhairi a nadin da zai taimaki ayyukan sanatan da Nijeriya baki daya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp