Home General Adadin kuɗin shigar Dangote zai kai dala biliyan 30 a shekara mai...

Adadin kuɗin shigar Dangote zai kai dala biliyan 30 a shekara mai zuwa

Fitaccen attajirin Nahiyar Afirka Aliko Dangote ya ce zai samu kuɗin shiga a dukkanin hada-hadar kasuwancisa da ta kai dala biliyan 30 a shekara mai zuwa, dukda yadda harajin Amurka zai shafi kamfanoninshi.

Shugaban rukunin kamfanonin na Dangote ya ce kasuwancinsa da suka haɗa da matatar man fetur mai ƙarfin tace ganga dubu 650 a kullum zai ƙaru da dala biliyan 5 a shekarar 2026.

Adadin kuɗin shigar kamfanonin na Dangote dai a wannan shekarar ya kai dala biliyan 25 abin da ke nufin idan an samu ƙarin dala biliyan 5 zai kama dala biliyan 30 a baɗi.

Shugaban Amurka Donlad Trump ya ware fannin mai da gas daga ƙarin haraji abin da ya sa matatar Dangote ci gaba da shigar da mai  a ƙasar. Baya ga haka Dangote na kai taki ƙasar ta Amurka.

Adadin harajin shigar da kaya da Najeriya ke biyan Amurka ya yi ƙasa da kashi 16 idan aka kwatanta da wanda Algeria ke biyan ƙasar, abin da ya bai wa ƙasar damar hada-hadar kasuwanci fiye da Algeria.

Dangote ya ce ya damu da harajin da Amurka ta sanya, saboda kashi 37 na takin da yake sayarwa na Urea yana zuwa Amurka ne. sai dai sun yi sa a ita ƙasar Algeria an ƙaƙaba mata kashi 30 na haraji.

A gefe guda kuma ana hasashen Dangote zai zama babban mai fitar da siminti a nahiyar Afirka a shekara mai zuwa, inda zai iya kere ƙasar Masar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp