Home General Tinubu zai gana da kamfanonin samar da lantarki kan bashin tiriliyan huɗu

Tinubu zai gana da kamfanonin samar da lantarki kan bashin tiriliyan huɗu

Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai gana da shugabanni na kamfanonin da ke samar da lantarki a ƙasar domin tattaunawa kan bashin naira tiriliyan huɗu da suke bi.

Wata sanarwa da mai magana da yawun Ministan Lantarki Adebayo Adelabu ya fitar ranar Lahadi ta ce gwamnatin tarayya “ta ƙagu ta shawo kan matsalar” bayan ganawar da ministan ya yi da shugaban kamfanonin ranar Talata.

Yayin ganawar, ministan ya tabbatar wa kamfanonin da ake kira Generation Companies (GenCos) cewa gwamnati za ta mayar da hankali wajen wani ɓangare na bashin, in ji sanarwar.

“Akwai buƙatar mu biya wani babban ɓangare na kuɗin kuɗi hannu, idan ya so daga baya sai mu nemi a yi mana lamuni na biyan ragowar nan gaba,” a cewar ministan kamar yadda Bolaji Tunji ya ruwaito cikin sanarwar.

Ta ƙara da cewa za a daddale abin da gwamnatin za ta biya ne yayin ganawar tsakanin shugaban ƙasa da shugabannin kamfanonin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp