Home General Gwamnatin Tinubu ta firgita da yunƙurin haɗaka – Atiku

Gwamnatin Tinubu ta firgita da yunƙurin haɗaka – Atiku

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta firgita da yunƙurin haɗakar jam’iyyun adawa inda ya ce har yanzu shi ne mafi ƙarfin ɗan adawa a Najeriya.

Ya bayyana hakan ne a matsayin martani ga kalaman Daniel Bwala, tsohon hadiminsa, wanda yanzu haka shi ne mai ba Shugaba Bola Ahmed Tinubu shawara kan harkokin sadarwar manufofi, inda ya shawarci Atiku da ya fasa ƙudirin sake tsayawa takara a 2027.

A wata hira da aka yi da shi a gidan talabiji na Channels, Bwala ya ce Atiku ya kamata ya yarda da ƙaddara, yana mai cewa wataƙila ba nufin Allah bane ya shugabanci Najeriya.

Ya kuma yi ikirarin cewa “Atiku ya rasa kashi 60 zuwa 70 cikin 100 na magoya bayansa, yana mai gargaɗin cewa ci gaba da wannan yunkuri na iya kai shi ga ƙarshe mai raɗaɗi.”

A martanin da ya fito daga ofishin yada labaran Atiku, an siffanta kalaman Bwala da “raini da kuma rashin mutunci,”.

Sanarwar ta ƙara da cewa “ceto da gina Najeriya aikin ne mai matuƙar muhimmanci na ƙasa — wanda bai kamata a bar shi yana tangal-tangal ba saboda son zuciyar wasu hadiman fadar shugaban ƙasa masu neman faranta ran kansu”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp