Home General Mayaƙan Boko Haram sun hana gudanar da Sallar Juma’ar a Kamaru

Mayaƙan Boko Haram sun hana gudanar da Sallar Juma’ar a Kamaru

Rahotanni daga ƙasar Kamaru sun ce barazanar kai harin mayakan Boko Haram a garin Garwa ya sanya hana Sallar Juma’ar da aka saba gudanarwa a yau, abin da ya jefa jama’a cikin ruɗani.

Bayanan sun ce tun da safe aka yi ta yaɗa labarin shirin kai harin ƴanta’addan, waɗanda suka zafafa hare-harensu a ƴan kwanakin nan, wannan ta sa shugabanni ɗaukar matakin dakatar da Sallar Juma’ar domin kare lafiyar jama’a.

Cikin manyan Masallatan da aka rufe yau har da Masallachin tsohon shugaban ƙasa Ahmadu Ahidjo.

Wakilin RFI hausa a Garwa Rilwanou Shehu Ousmane ya tabbatar da aukuwar lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp