Home General Birtaniya ta yaba wa Tinubu kan tsare-tsaren tattalin arziƙi

Birtaniya ta yaba wa Tinubu kan tsare-tsaren tattalin arziƙi

Gwamnatin Birtaniya ta ce matakan da shugaban Najeriya bola Ahmed Tinubu ke ɗauka a ɓangaren tattalin arzikin ƙasar kwalliya na biyan kuɗin sabulu.

Birtaniyan ta ce matakan da aka ɗauka musamman wajen farfaɗo da darajar kuɗin ƙasar, da na kuɗin shiga na daga cikin dalilan da suka aka samu ƙaruwar damar zuba jari a ƙasar.

Jakadan Birtaniya a Najeriya Dr. Richard Montgomery ne ya sanar da hakan a yayin wani taro na aiwatar da shirin bunƙasa tattalin arzikin Najeriya da Birtaniya, ta fuskar kasuwanci da zuba jari tsakanin ƙasashen biyu, da ya gudana a Abuja babban birnin na Najeriya.

Gwamnatin Birtaniyar ta ce la’akari da rahoton da Bankin Duniya a baya-bayan nan kan harkokin zuba jari a Najeriya ya nuna cewar darajar kuɗin ƙasar naira na farfaɗowa.

Haka kuma rahoton ya ce ana samun ƙaruwar kuɗaɗe a asusun ƙasashen wajen na ƙasar da kuma na haraji, lamarin da ya sa ake samun buƙatar ƙara faɗaɗa harkokin zuba jari a ƙasar.

Birtaniyan ta ce shirin bunƙasa tattalin arzikin ƙasashen biyu da suke haɗin gwiwa za a cimma shi ne idan Najeriya ta mayar da hankali kan wajen samar da daidaitacen tsari da zai haɓaka harkokin kasuwanci da janyo hankulan masu zuba jari a ƙasar.

Sai dai ya ce ganin irin matakan da shugaban Najeriya ya ɗauka a ɓangaren tattalin arzikin ƙasar, yasa suka fitar da wasu ɓanagarori takwas da zasu haɗa gwiwa da Najeriya wajen ganin ta haɓaka kasuwacin da yawan masu zuba jari a ƙasar.

Haka kuma Jakadan Birtaniyar ya ce baiwa kamfanonin ƙasar irin na su Ɗangote suka fara tace man fetur yasa an samu raguwar fitar da ɗanyen man fetur zuwa ƙasashen waje.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp