Home Labarai Gwamnatin Tinubu ta jefa ƴan Najeriya fiye da miliyan 150 cikin tsananin...

Gwamnatin Tinubu ta jefa ƴan Najeriya fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ke cika shekara biyu da soma wa’adin mulkinta na farko, hadaddiyar kungiyar kwadagon kasar ta NLC ta bayyana gwamnatin a matsayin wadda ta kasa cika alkawarrun da ta dauka a bangarori da dama.

Kungiyar ta NLC ta ce ikirarin shugaban kasar na cewa lokacin wahalar rayuwa ya zo karshe, na tamkar yaudara ce kasancewar manufofi da tsare-tsaren gwamnatin sun jefa fiye da ‘yan Najeriya miliyan 150 a cikin tsananin talauci da tsadar rayuwa.

A cikin wani bayani da ta fitar, Kungiyar kwadagon ta Najeriya ta bakin shugabanta Kwamared Joe Ajaero ya ce babu komi a cikin tafiyar wannan gwamnati face maimaita gazawar da gwamnatin da ta gada ta yi ne musamman a bangaren sabunta fata da manufofi.

To sai dai jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, ta mayar da martini ga kungiyar ta kwadago ta NLC, inda ta ce babu adalci a maganar ‘yan kwadagon sannan ba su yi bincike mai zurfi ba, kafin furta wadannan kalamai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp