Home General Sojojin Najeriya sun kashe manyan kwamandojin Boko Haram da ISWAP

Sojojin Najeriya sun kashe manyan kwamandojin Boko Haram da ISWAP

Nigerian Army

Rundunar sojojin Najeriya ta samu gagarumar nasarar kashe manyan manyan kwamandojin Boko Haram da na tsagin ISWAP, a wasu hare-hare da ta kai a makon da ya gabata da kuma wannan makon da mu ke ciki.

A wasu hare-hare da sojojin da ke aiki a ƙarƙashin rundunar Operation Hadin Kai suka kai garuruwan Mallam Fatori da kuma Buratai na jihar Borno a makon da ya gabata, sun samu nasarar kashe kwamandojin Boko Haram uku da suka haɗa da Amir Abu Ali da Amir Ibunu sai kuma Amir Abu Waldume.

Haka nan a wani harin na daban da suka kai Nzalgana na jihar Yobe da kuma Timbuktu na jihar Borno, jami’an tsaron na Najeriya sun kashe Ameer Malam Jidda, ɗaya daga cikin manyan kwamandojin Boko Haram a garin Ngorgore da Malumti.

Kisan manyan jagororin Boko Haram da sojojin Najeriya suka dai ya raunata tsarin shugabancinsu da kuma sanyasu cikin ɗimuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp