Home General Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin kwashe ƴan ƙasarta daga Iran

Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin kwashe ƴan ƙasarta daga Iran

Bola Ahned Tinubu

Gwamnatin Najeriya ta yi watsi da zargin yin biris da ƴan ƙasarta dake Iran dai-dai lokacin da yaƙi ke ƙara rinchaɓewa a tsakanin Isra’ila da Iran ɗin.

A wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Kimiebi Imomotimi Ebienfa ta ce zargin bashi da tsuhe ballantana makama.

A cewar sanarwar gwamnatin Najeriya, ƙarƙashin ma’aikatar harkokin waje na iya bakin ƙoƙarinta don tabbatar da cewa ƴan Najeriya mazauna Tehran na cikin ƙoshin lafiya.

Sanarwar ta ci gaba da cewa an baiwa ma’aikatan da ke yiwa gwamnatin Najeriya aiki a Iran damar aiki daga gida, sakamakon hare-haren da ke faɗawa sassan birnin.

Ma’aikatar harkokin wajen ta kuma ƙara da cewa tuni gwamnati ta fara aiki tare da gwamnatin Armenia don duba yadda ƴan Najeriya mazauna Iran ɗin zasu tsallaka ƙasar don samun mafaka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp