Home General NNPCL ya ƙara farashin litar man fetur

NNPCL ya ƙara farashin litar man fetur

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin litar mai daga naira 910 zuwa naira 945 a gidajen mansa da ke Abuja, babban birnin ƙasar.

Haka kuma kamfanin ya ƙara farashin litar mai a gidajen mansa da ke Legas daga naira 870 zuwa 915, kamar yadda rahotanni suka nuna.

Wannan ƙarin ya nuna an ƙara naira 35 a kowace lita a Abuja, da kuma ƙarin naira 45 a Legas.

Jaridar Daily Trust mai zaman kanta ta ruwaito cewa tuni wasu gidajen man suka fara sayar da fetur ɗin a sabon farahi, inda ta ruwaito gidan man NNPCL da ke babbar hanyar Fin Niger Badagry ya fara sayar da man a naira 915.

Haka kuma a gidan man kamfanin NNPCL da ke yankin Kubwa na Abuja, tuni aka fara sayar da man a naira 945.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp