Home General Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki don hana sake faruwar kisan mutane a jihar bayan kisan wasu ƴan asalin jihar Kaduna a ƙaramar hukumar Mangu da ke jihar.

A makon jiya ne dai aka kashe wasu matafiya 12 ƴan Zaria, da ba su ji ba su gani ba, wani abu da ya janyo Allah-wadai daga ɓangarori daban-daban.

Joyce Ramnav, ita ce kwamishiniyar watsa labarai a jihar ta Filato, ta bayyanawa BBC cewa burinsu shi ne su nuna wa duniya cewa Filato jiha ce mai son zaman lafiya, mai maraba da mutane.

Ta ce, “jami’an tsaron sun kama mutum 22, kuma idan allah ya yarda gwamnati za ta ɗauki matakin domin a tabbatar an hukunta waɗannan mutane.”

Ta ce yanzu gwamnati na jiran sakamakon bincike ne da ƴansandan jihar ke gabatarwa, “kafin mu san matakin da za mu ɗauka na gaba.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp