Home General Gwamnatin jihar Kano ta yi Alla-wadai da kisan ‘yan asalin jihar a...

Gwamnatin jihar Kano ta yi Alla-wadai da kisan ‘yan asalin jihar a Benuwai

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba kabir Yusuf ya yi Alla-wadai da kisan matasa ‘yan asalin jihar a garin makurdi dake jihar Benuwai.
Wannan na cikin wata takardar sanarwa da Mai Magana da yawan Gwamnan kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, Sanusi Bature Dawakin Tofa  ya fitar aka raba manema labarai a jihar Kano.
Sanarwar ta ce lamarin ya auku ga Matasan ne da misalin karfe 11: na daren litinin wanda kawo yanzu ba a kai ga gano wadanda suka aikata wannan aika-aikar ba.
Cikin bakin cikin gwamnan Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana kisan na rashin imani matsayin rashin hankali, wanda kuma ba za a lamunta ba.
Tun da fari dai an ruwaito matasan biyu da suka haɗar da Barham Sulaiman da Jamilu Ahmad ƴan asalin unguwa uku ne a jihar Kano.
Daga bisani sanarwa ta ce Gwamnan zai jagorancin wata tawagar ciki har da iyayen matasan domin gudanar da Jana’izarsu a babban masallacin ƙasa dake birnin Abuja.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp