Home General Gwamnatin jihar Kano ta yi Alla-wadai da kisan ‘yan asalin jihar a...

Gwamnatin jihar Kano ta yi Alla-wadai da kisan ‘yan asalin jihar a Benuwai

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba kabir Yusuf ya yi Alla-wadai da kisan matasa ‘yan asalin jihar a garin makurdi dake jihar Benuwai.
Wannan na cikin wata takardar sanarwa da Mai Magana da yawan Gwamnan kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, Sanusi Bature Dawakin Tofa  ya fitar aka raba manema labarai a jihar Kano.
Sanarwar ta ce lamarin ya auku ga Matasan ne da misalin karfe 11: na daren litinin wanda kawo yanzu ba a kai ga gano wadanda suka aikata wannan aika-aikar ba.
Cikin bakin cikin gwamnan Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana kisan na rashin imani matsayin rashin hankali, wanda kuma ba za a lamunta ba.
Tun da fari dai an ruwaito matasan biyu da suka haɗar da Barham Sulaiman da Jamilu Ahmad ƴan asalin unguwa uku ne a jihar Kano.
Daga bisani sanarwa ta ce Gwamnan zai jagorancin wata tawagar ciki har da iyayen matasan domin gudanar da Jana’izarsu a babban masallacin ƙasa dake birnin Abuja.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp