Home General Ƴanbindiga sun hallaka ƴan banga a jihar Filato

Ƴanbindiga sun hallaka ƴan banga a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato da ke tsakiyar Najeriya na cewa ƴanbindiga sun kai harin kwanto ɓauna kan wasu ƴan banga tare da kashe aƙalla 70 a wasu ƙauyukan jihar biyu.

Wani mazaunin garin Kukawa da ke jihar na cewa fiye da ƴan banga 60 aka kashe a garin.

Can ma a ƙauyen Banyun na jihar wani mazaunin yankin ya tabbatar wa jaridar kashe ƴan banga 10.

Ya ƙara da cewa maharan sun kuma ƙona gidaje da dama da dukiyoyi.

Bayanai na cewa tun bayan da hare-hare suka yawaita a wasu yankunan Wase, aka riƙa gayyato ƴan banga daga wasu yankunan jihar da ma jihar Taraba domin taimaka wa tsaron wasu ƙauyukan yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp