Home Labarai Ƴanbindiga sun sake kashe manoma 27 a harin da suka kai jihar...

Ƴanbindiga sun sake kashe manoma 27 a harin da suka kai jihar Filato

‘Yan bindiga sun kai wani sabon hari a ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Filato, tare da kashe aƙalla manoma 27, a wani yanayi da hare-hare ke ci gaba da zafafa a jihar ta Arewacin Najeriya.

sun bayyana cewa tuni aka garzaya da mutanen da suka tsira da raunuka zuwa asibitin koyarwa na garin Jos da kuma sauran wasu asibitocin a cikin jihar.

Dalyop Solomon, shugaban ƙungiyar matasan Birom ta BYM ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin, a cewarsa maharan sun kutsa yankin ne wurin ƙarfe 5:30 na Asuba a ranar Litinin, inda suka fara harbi kan mai uwa da wabi tare da cinnawa gidaje wuta.

Shugaban ya tabbatar da mutuwar mutane 27, inda ya ce za’a sanar da lokacin jana’izarsu nan gaba, yayin da da dama suka jikkata kuma aka garzaya dasu asibiti.

Tuni ƙungiyar makiyaya ta Miyetti Allah ta barranta kanta daga harin.

Shugaban ƙungiyar na Filato, Ibrahim Babayo ya ce ko kusa basu da hannu a kai harin, yana mai cewa zarginsu da ake bashi da tushe ballantana makama.

Har zuwa wannan lokaci dai gwamnati ba ta ce komai kan harin ba, a wani yanayi da jihar ta tsakiyar arewacin Najeriya ke ci gaba da fama da rikice-rikice da ke haddasa asarar ɗimbin rayuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp