Home Labarai Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya

Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya

Shugabn Nijeriya Bola Tinubu ya karawa shugaban hukumar hana fasa kwauri ta kasa (Custom) Bashir Adewale Adeniyi wa’adin aiki na shekara guda.

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da wa’adin aikin nasa zai kare karshen wata mai kamawa wato 31 ga watan Agustan 2025.

Ta cikin wata sanarwa daga Fadar Shugaban Ƙasa da Bayo Onanuga, Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan Harkokin Bayani da Tsare-tsare, ya sanya wa hannu, wadda ta ce ƙarin wa’adin na da nufin bai wa Adeniyi damar kammala sauye-sauyen da ake aiwatarwa tare da cika manyan manufofin gwamnatin Bola Tinubu.

Ayyukan  da ake son kammalawa sun haɗa da sabunta tsarin aikin Hukumar Kwastam, aiwatar da tsarin National Single Window Project, da kuma cika alƙawarin da Najeriya ta ɗauka a ƙarƙashin yarjejeniyar ciniki ta nahiyar Afirka (AfCFTA).

Shugaba Tinubu ya yabawa Adeniyi bisa “ƙwazo da ya nuna wajen jagoranci da da kuma hidimatawa,” yana mai bayyana tabbacin cewa ƙarin wa’adin zai ƙarfafa rawar da Hukumar Kwastam ke takawa a fannin sauƙaƙe cinikayya, haɓaka kuɗaɗen shiga, da kuma tsaro a kan iyakoki Nijeriya.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp