Home Labarai Dino Melaye ya koma jam’iyyar ADC bayan ficewarsa daga PDP

Dino Melaye ya koma jam’iyyar ADC bayan ficewarsa daga PDP

Tsohon ɗan jamalisar dattawan Najeriya mai wakiltar Kogi ta Yamma ya koma jam’iyyar haɗakar ADC bayan ficewarsa daga PDP.

Cikin wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na X, an ga yadda Dino Melaye ya karɓi katin jam’iyyar ADC daga hannun jagororin jam’iyyar na ƙaramar hukumarsa.

Tun da farko a yau ne Dino Melaye ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP bayan ya rubuta wa jagororin jam’iyyar na mazaɓarsa ta Aiyetoro Gbede wasiƙar ficewarsa daga jam’iyyar.

A cikin wasiƙar Melaye ya bayyana dalilan kasawar jam’iyyar wajen magance matsalolin da ke damunta.

”Matakin ya zama wajibi saboda gazawar jam’iyyar wajen ceto yan Najeriya daga cikin kuncin da ƙasarmu ke ciki”, kamar yadda wasiƙar ta bayyana.

Tsohon ɗan takarar gwamnan jihar Kogin na jam’iyyar PDP ya ce ya ɗauki matakin ne bayan dogon nazari kan halin da jam’iyyar ke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp