Home Labarai Ƙananan dillalan mai sun zargi shugabanninsu da yiwa Matatar Dangote zagon ƙasa

Ƙananan dillalan mai sun zargi shugabanninsu da yiwa Matatar Dangote zagon ƙasa

Matatar Dangote

Ƙananan dillalan man fetur a Najeriya sun zargi shugabannin su da neman yiwa Matatar Dangote zagon ƙasa a yunƙurin ta na jigila da kuma rarraba tataccen mai zuwa sassan ƙasar.

Daya daga cikin ƙananan dillalan Alhaji Ladan Abdullahi Garkuwa ya ce matakin na Dangote zai bai wa masu ƙaramin ƙarfi irin su damar dawo da karsashin su na dillancin man, la’akari da cewar tsadar man ya sa basa iya sayensa kamar yadda suke yi a baya.

Garkuwa ya ce da yana da gidajen mai guda biyar yanzu haka, amma tsadarsa ya sa ba ya iya sayen mota guda da zai sayar.

Dillalin ya ce yanzu da wannan sabon tsari na Dangote wanda zai dinga kai musu man kai tsaye zuwa gidajen man su, inda har sai sun sayar su biya shi, matakin zai ba shi damar karbar man a gidajen man sa guda biyar domin ci gaba da kasuwancinsa.

Dan kasuwan ya ce wannan mataki zai ba shi damar ɗaukar ƙarin ma’aikata waɗanda su ma za su amfana da tsarin, wadda za ta taimaka wajen sauƙaƙa wahalar man.garkuwa ya ce abin takaici ne yadda manyan dilallan man ke adawa da shirin Dangoten, wanda suke kallonsa a matsayin babbar barazana ga harkokin su, musamman  ganin yadda suka mamaye harkar man suke kuma cin karen su babu babbaka.

Tuni matatar Dangote ta karɓi wasu daga cikin motocin da ta sayo daga ƙasar China da za su yi aikin jigilar man zuwa sassan Najeriya, a yunƙurin sauƙaƙawa jama’ar ƙasar samun tacaccen man da suke sarrafawa.

A baya, manyan dillalan man a Najeriya, sun gabatar da ƙorafin adawa da shirin Dangote na sayo motocin da za su dinga safarar man, inda suka zarge shi da yunƙurin mamaye kasuwar.

Wanan bai sanya Dangoten ƙasa a gwuiwa ba, wajen ci gaba da sayo motocin waɗanda tuni suka isa Najeriya domin fara aiki.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp